Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Adamawa ta ayyana kwanaki 3 a matsayin ranakun zaman makokin Abdulrahman Abba

Published

on

Gwamnatin Jihar Adamawa ta ayyana kwanaki uku a matsayin ranakun zaman makoki, sakamakon mutuwar shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Jihar Abdulrahman Abba Jimeta, a safiyar yau a kasa mai tsarki bayan zuwa domin Umara.

Zaman makokin dai ya fara ne daga yau Litinin 18 ga watan Yuni zuwa Laraba 21 ga wata, kuma za a yi jana’izarsa a can kasa masallacin Harami da ke kasa tsarki wato Saudiyya da karfe biyu na ranar yau agogon Najeriya, kuma karfe hudu agogon Saudiyya.

Wata sanarwa mai dauke da sa-hannun kwamishina yada labaran Jihar  Ahmed Sajoh, ta ce gwamnan Jihar Muhammad Umar Bindow ya bukaci al’ummar Jihar su yi wa marigayin addu’ar neman gafara.

Abdulrahman Abba Jimeta ya rasu yana da shekaru 60, ya kuma bar mahaifinsa da mata guda da kuma ‘ya’ya 11.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!