Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta dauki gabaran tattaunawa da kungiyar Bokon haram

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnatin sa ta dauki gabaran tattaunawa da kungiyar Boko-Haram domin ceto ‘yan matan Sakandaren Dapchi wadanda aka sace su a makarantar su a kwanakin baya.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Femi Adesina ya bayar jiya a Abuja.

 

A cewar sanarwar, shugaba Buhari ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke maraba ga sakataren harkokin wajen Amurka Mr. Rex Tillerson a fadar shugaban kasa ta Asorok da ke Abuja.

 

Sanarwar ta kuma ruwaito cewa tuni gwamnatin tarayya ta tuntubi kungiyoyin kasa da kasa da masu shiga tsakani domin tattaunawa kan hanyoyin da za a bi wajen sakin ‘yan matan.

 

Shugaba Buhari ta cikin sanarwar dai ya kara da cewa a cikin makwannan zai kai ziyara makarantar da lamarin ya faru domin jajantawa iyayen yaran.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!