Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar aikin hajji ta kasa ta fitar da wasu lambobin tuntuba

Published

on

Hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta ce ta fitar da wasu lambobin da za a dinga tuntubar ta, ga dukkanin wani da ke da korafi kan yadda aikin Umara ke gudana a halin yanzu.

 

Rahotanni dai na nuni da cewa al’umma da dama ne ke zube a filin jirgin saman garin Makka da kuma Jidda wadanda kamfanoni da suka kai su suka zubar da su.

 

Cikin wata sanarwa da hukumar ta NAHCON ta fitar a jiya Laraba ta bakin jami’ar yada labaran hukumar Fatima Usara ta ce a kokarin da hukumar ke yi na kaucewa samun matsala tuni hukumar ta aike da ma’aikatan ta zuwa kasar ta Saudiyya domin duba halin da al’umma ke ciki.

 

Haka kuma hukumar ta NAHCON ta bukaci dukkanin wadanda ke da korafi da su tuntubi jami’an hukumar a wurare daban daban da aka ajiye su ko kuma Jami ‘anta da ke shalkwatar hukumar ta NAHCON da ke Jiddah.

 

Hukumar ta NAHCON ta kuma shawara ci wadanda suka gudanar da ayyukan Umrah a bana da suyi kokari kada su ketare kwanakin da aka diba musu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!