Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

NCC:wayar salula fiye da miliyan casa’in ne basu da rijistan layukansu

Published

on

Hukumar kula da kafofin sadarwa ta kasa (NCC), ta ce, masu amfani da wayar salula miliyan casa’in da biyar da dubu dari bakwai ne basu da cikakken rajistar layukan wayar salular su a kasar nan.

 

A cewar hukumar lamarin ya faru ne sakamakon rashin daukar cikakken bayanan su ta hanyar dangwala yatsa da kuma hoton fuskar su, watakila saboda tangardar na’ura.

 

Hukumar NCC ta kuma ce, nan gaba ba da dadewa ba, za ta aika da sakon text ga masu wadannan layukan tarho da su je su yi cikakken rajistar layukansu.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar jiya a Abuja wanda aka rabawa manema labarai.

Sanarwar ta ce, kwamishina mai kula da harkokin masu ruwa da tsaki a hukumar Mr. Sunday Dare ne ya bayyana haka, yayin wani taron karawa juna sani a garin Fatakwal babban birnin jihar Rivers.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!