Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kano: An karrama jami’an lafiya

Published

on

Shugaban sashen lafiya na karamar hukumar Tofa Alhaji Adda’u Ubale Rano, ya yi kira ga dukkanin ma’aikatan lafiya dake karkashinsa da su kara zage dantse wajen maida hankali kan ayyukansu domin kara samun nasara a dukkan ayyukan da suka sanya a gaba.

Alhaji Adda’u Ubale Rano ya bayyana hakan ne yayin da yake mika kyautuka ga wasu daga cikin ma’aikatan wadanda suke bangaren bada allurar rigakafi bisa irin jajircewar da suka yi yayin gudanar da allurar rigakafin.

Ya kara da cewa, karamar hukumar Tofa ta dade a mataki na kasa a fannin alluran rigakafi amma bisa dagewar da ma’aikatan suka yi a wannan lokaci karamar hukumar ta dawo mataki na biyun farko a fadin jihar Kano.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/11/TRACK-UP-H-GIFT-A-15-11-2019.mp3?_=1

A nata bangaren mataimakiyar Shugaban da ke lura da allurar rigakafin shiyyar Dawakin Tofa Hajiya Zullaiha Ahmad ta bayyana irin jajecewar da Adda’u Ranon ya yi wajen ganin karamar hukumar ta haura zuwa mataki na gaba da.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/11/TRACK-UP-H-GIFT-B-15-11-2019.mp3?_=2

Wakilinmu Umar Lawan Tofa ya rawaito cewa a yayin taron Alhaji Abdu Umar da yawakilci Hakimin Tofa da sauran dagatai sun bayyana jin dadin su bisa nasarar da karamar hukumar ta samu ta zuwa mataki na gaba a bangaren kiwon lafiya.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!