Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wajibi iyaye su tashi tsaye wajen tarbiyar ‘ya’yan su -Sarkin Alkalma

Published

on

Sarkin Alkalman Kano Alhaji Iliyasu Labaran Daneji yace matukar Iyaye suna so a magance matsalar tabarbarewar tarbiyyar ‘ya’ya a wannan zamani ya zama wajibi iyaye su tashi tsaye wajen ganin yaran su sun sami ingantaccen Ilimin Addinin musulunci.

Alhaji Ilyasu Daneji ya bayyana hakan ne lokacin saukar Karatun Al’qur’ani mai girma karo na biyu na Makarantar Shabbabu Rasulillah Islamiyya dake Unguwar Nalado dake Tukuntawa a yankin Burnin Kano.

Sarkin Alkalman Kano Alhaji Ilyasu Daneji ya kara da cewa abun takaici ne yadda tarbiyya a yanzu tayi karanci a tsakanin matasa wanda hakan ke da nasaba da rashin tsayawar iyaye kai-da-fata-wajen sanya ‘ya’yan su a makaranta domin neman Ilimi.

Da yake jawabi shugaban Makarantar Malam Musbahu Saleh kira yayi ga masu hannu da shuni dasu kawowa makarantar dauki kasancewar makarantar ta shafe sama da shekaru 27 a duniya amma har yanzu bata dena fuskantar matsalar rashin abun zama da muhalli ba.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa malamai da dama ne suka halarci taron bikin saukar da sauran al’ummar gari na dalibai bakwai maza da mata wanda suka sami damar sauke karatun Al’kur’ani mai girma a makarantar a yau.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!