Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Kalubale na na farko a masana’antar Kanny Wood shine kin amincewar Iyaye–Rukayya Dawayya

Published

on

Fitacciyar jaruma kuma mai daukar nauyin fina-finai wato Rukayya Umar Santa wadda aka fi sani da Dawayya ta bayyana cewa ta samu nasarori da dama a zamanta a masana’antar Kannywood.

Yayin wata tattaunawa da tayi da Freedom Radio ta bayyana cewa ta samu nasarori da dama a rayuwarta cikin sama da shekaru goma sha biyar da ta shafe a masana’antar.

Dawayya ta ce babbar kalubalen data fuskanta kafin ta shigo masana’antar shi ne rashin yarjewar iyayen ta, domin kuwa a farko sun nuna rashin amincewar su kafin daga bisani  suka amince.

Ta kara da cewa ta samu cigaba matuka tun sanda  tazo masana’antar Kannywood a farko.

A karshe jaruma Dawayya ta mika sakon godiya ga masoyanta bisa addu’oi da goyan bayansu gareta.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!