Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Kashi 50 na cin zarafin dan Adam na faruwa ne a matakin Iyali

Published

on

Hukumar kare hakkin dan Adam ta kasa dake nan Kano tace yawancin rahotanni da suke samu na cin zarafin bil’ Adam ana faruwa ne a gidaje.

Shugaban hukumar kare hakkin dan Adam na Jahar Kano Shehu Abdullahi ne ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da filin Barka da Hantsi a cikin bikin ranar kare hakkin dan Adam ta Duniya da ake bikin a yau.

Tun a ranar 10 ga watan Disambar 1948 ne majalisar dinkin Duniya ta ware domin kare hakkin dan Adam.

A nasa bangaren shugaban gamayyar kungiyoyin kare hakkin dan Adam ta Jahar Kano Kwamared Abdullahi Haruna Ayagi yace kokarin da kungiyar su take yi na kare hakkin dan Adam shi ne wayar da kan al’umma da kuma koyar da yara kanana matsalolin rayuwa.

Yace idan sun samu labarin cin zarafi suna hada kai da hukumar ‘’Yansanda da sauran jami’an tsaro domin magance matsalar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!