Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ku kasance masu yin kasuwanci kamar yadda addinin musulunci ya koyar

Published

on

An shawarci ‘yan kasuwa da sauran ma’aikata da su kasance masu gudanar da harkokin kasuwancinsu irin yadda  addinin musulunci ya koyar domin kaucewa fadawa cikin fushin ubangiji a ranar gobe kiyama.

Shugaban cibiyar koyar da zaman Aure da kasuwanci a addinin Musulunci Dakta Yahya Tanko ne ya bayyana hakan yau lokacin taron bita tare da wayar da kan ‘yan kasuwa da ma’aikata kan tarbiyyar addinin musulunci a cikin harkokin kasuwanci.

Ya kara da cewa abin takaici ne yadda ‘yan kasuwa a yanzu suke gudanar da harkokin kasuwancin su, wanda hakan ya sauka daga layin koyarwa irin ta addinin musulunci.

A cewar Dakta Yahya Tanko kamata ya yi duk wani musulmi a ko ina yake ya zama tamkar mudubi da kowacce al’umma zata rika koyi da shi ta fuskar kasuwanci.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa malamai da ‘yan kasuwa da ma’aikata da dama ne suke halarci taron.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!