Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Masu Adaidaita sahu sun roki gwamnatin Kano kar ta sanya musu haraji

Published

on

Gamayyar kungiyoyin masu baburan Adaidaita sahu na jihar Kano, sun yi Kira ga gwamnatin jihar Kano, da ta sassuta musu, ko ta rage kudin harajin da ta ke kokarin sanya musu.

Mataimakin sakataren gamayyar kungiyoyin, Malam Suleiman Mu’azu ne yayi wannan kiran, yayin wata ziyara da suka kawo tashar freedom rediyo da safiyar yau.

Ya ce, ya kamata gwamnati ta yi la’akari da halin matsin tattalin arzki  da ake ciki, kafin daukar wannan mataki.

Daya daga cikin mambar kungiyar mai suna Nazifi Shu’aibu, cewa ya yi, ya kamata gwamnati ta dawo da kudin zuwa dubu goma ko biyar ko takwas ko kuma kasa da haka.

Kungiyoyin dai sun ce matukar gwannati ta ki yin la’akari da halin da suke ciki wajen rage kudin, ba kuwa ko shakka da dama daga mambobinsu za su tagayyara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!