Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Yakamata a’lumma su siffanta da dabi’ar kunya-Limamin Zam-zam

Published

on

Limamin masallacin Juma’a na Zam-Zam karkashin cibiyar addinin musulunci ta Jama’atul Wa’azu wal Irshad dake Hotoro Tsamiyar Boka Malam Muhammad Sani Amin Idris ya ja hankalin al’ummar musulmi wajen siffanta da ta’adar kunya a harkokin su na yau da kullum.

Malam Muhammad Sani Amin Idris wanda na daya daga cikin limamin masallacin Juma’a na Zam-Zam ya bayyana hakan ne yayin Hudubar Sallar Juma’a da ya gabatar.

Ya ce shakka babu dabi’antuwa da kunya kai ya taimakawa wajen kyautata lamura a tsakanin al’umma.

Ya kuma kara da cewa akwai bukatar iyaye da sauran magabata su dage wajen kimsawa ‘ya’yan su dabi’u masu kyau a wani bangare na samar da ingantacciyar al’umma ana gaba.

Mahukunta su mai da hankali kan al’umma -Limami

Limamin jumu’a a Kano yayi Allah-wadai da “Black Friday”

Wakilin mu Umar Idris Shuaibu ya ruwaito limamin Malam Muhammad Sani Amin Idris ya ce ba a bukatar kunya a abubuwan da suka shafi addini, wanda zata haifar da rashin aikata koyarwar annabin tsira Muhammad (S.A.W).

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!