Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Gwamantin Kano ta kaddamar da kwamitin bunkasa harkokin noma

Published

on

Gwamnatin Kano ta kaddamar da kwamitin mutane 20 na shirin bunkasa noma da kiwo a jihar.

Shirin dai zai lakume Dala Milyan 95 wanda kuma tallafi ne daga Bankin musulunci dake kasar Saudiyya.

Shirin dai zai mayar da hankali ne kan bunkasa harkokin noma da kiwon dabbobi, da nufin dakile matsalar talauci da kuma samar da wadataccen abinci.

Wannan na cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a dake kula da shirin Ameen Yassar ya fitar.

Ta cikin sanarwar dai, Mataimakin Gwamnan Kano Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna yayin kaddamar da kwamitin, ya ce,  shakka babu shirin zai taimaka gaya wajen ci gaban daukacin bangaren noma da kiwon dabbobi.

Ya kara da cewa shirin zai bunkasa rayuwar mutane kimanin fiye da milyan daya a daukacin kananan hukumomin jihar 44.

Mataimakin Gwamnan Kano Nasiru Yusuf Gawuna wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar gona Malam Adamu Abdu Faragai, ya ce, shirin zai kuma taimaka wajen magance matsalolin rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya da ake samu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!