Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya jajantawa alummar Garkida

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajantawa al’ummar kauyen Garkida na jihar Adamawa da kungiyar Boko Haram ta kaiwa hari.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai Garba Shehu ya fitar jiya a birnin tarayya Abuja.

Ta cikin sanarwar, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce shakka babu sojojin kasar nan sun mai da hankali kan rage wa mayakan Boko Haram karfi a yankunan arewa maso gabashin kasar nan.

Shugaba Buhari ya ce ya zama wajibi a yabawa jami’an tsaron kasar nan kan yadda suke aiki ba dare ba rana wajen tabbatar da zaman lafiya.

Yaki da cin hanci da rashawa bana Buhari ba ne- Ministan Ruwa

Buhari Bai Damu Da Harkokin Lafiya Ba-Likitocin Yara

Shugaba Buhari ya gana da sufeton yan sanda ta kasa kan arangamar yan Shi’a

Muhammadu Buhari ya kara da cewa, nan da wani dan lokaci Gwamnati zata kaddamar da kamfe kan yakar ta’addanci.

Shugaban kasa ya kuma yi kira ga al’ummar kasar nan wajen ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon baya na kare dukiya da tsaron lafiyar ‘yan kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!