Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Gwamnatin Najeriya ta zabi Gbenga Elegbeleye a matsayin wanda zai jagoranci ‘yan-wasa a winter Olympics

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta zabe tsohon Babban Daraktan kwamitin wasanni na kasa Gbenga Elegbeleye, a matsayin wanda zai jagoranci ‘yan-wasa a gasar winter Olympics da za’a gudanar a Pyeong Chang na kasar Koriya ta Kudu, wanda za’ a fara ranar 9 zuwa 28 ga watan Fabrairu mai ka mawa.

shugaban kwamitin Olympics na kasa, Habu Gumel ne ya bayyana hakan a jiya a taron karrama wasu ‘yan-wasan Olympics din kasar nan da ya gudana a birnin tarayya Abuja.

Shugaban hukumar Olympics din Habu Gumel ya ce sauran yan wasan da suke zama a kasar Amurka zasu shigo Najeriya a ranar Larabar nan daga nan su tashi zuwa kasar Koriya ta kudu.

‘yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle mata hudu ne za su wakilci Najeriya a gasar wadanda da suka hadar da Simidele Adeagbo da Seun Adigun da Ngozi Onwueme da kuma Akuoma Omeoga.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!