Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

COVID-19 An dage gasar cin kofin Nahiyar Afirka

Published

on

Hukumar shirya gasar cin kofin Nahiyar Afirka CAF ta sanar da dage gasar da za a yi a shekarar 2021 zuwa watan Janairun 2022.

Hukumar ta ce matakin ya biyo bayan annobar Covid-19 da ake fama da ita da ta addabi duniya.

Tun farko an tsara gudanar da gasar cin kofin Afirka a watan Janairun shekarar 2021.

Haka zalika hukumar CAF ta sanar da cewa an dage gasar cin kofin nahiyar Afirka na kungiyoyin da ke taka leda a cikin gida wato CHAN da aka tsara za a yi a watan Afrilu, yanzu haka dai an shirya gudanar da gasar a watan Janairun 2021.

Kasar Kamaru ce dai zata karbi bakuncin wasannin da za a yi na gasar cin kofin Afirkan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!