Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Garkuwa da mutane: An sace ɗaliban sakandire a Jihar Kaduna

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari makarantar Saint Albert College Kagoma, dake ƙaramar hukumar Jama’a a ranar Litinin, inda sukayi awon gaba da dalibai uku.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ASP Muhd Jalige ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Talata.
Ya kuma ƙara da cewa, daga shigar ƴan bindigar harabar makarantar ne suka fara harbe-harbe, inda suka raunata wasu ɗaliban tare da yin garkuwa da guda uku.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan ya yabawa mutane, musamman yadda suke baiwa rundunar rahotannin sirri wanda yake taimaka musu wajen gudanarda ayyukan magance matsalar rashin tsaro a jihar Kaduna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!