Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Rashin tsaro: An sanya dokar taƙaita zirga-zirga a Kaduna

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta ayyana dokar takaita zirga-zirga na tsawon sa’o’i 24 a ƙananan hukumomin Jema’a da Kauru.

Wannan dai ya biyo bayan shawarar da hukumomin tsaro a jihar suka bayar don inganta tsaro a yankunan.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida ta jihar Samuel Aruwan ya fitar ta ce, sanya dokar taƙaita zirga-zirgar zai baiwa jami’an tsaro damar gudanar da ayyukan su na wanzar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Haka kuma jami’an tsaro za su sanya ido don ganin al’ummar yankunan su bi dokar.

Sanarwar takuma buƙaci su da su baiwa jami’an tsaron haɗin kai wajen gudanar da ayyukan su domin dawo da zaman lafiya a yankunan.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!