Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaban kwalejin fasaha ta Kano ya musanta zargin da ake yi musu

Published

on

Shugaban kwalejin kimiyya da fasaha ta Polytechnic Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa ya musanta zargin da kungiyar malaman kwalejin ta ASUP da kungiyoyin dalibai suka yi na cefanar da wasu filaye mallakin makarantar.

Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa ya bayyana hakan ne yau, jim kadan bayan wata zanga-zangar lumana da ta wakana da safiyar yau a harabar makarantar, a wani mataki na nuna fushin su kan zargin da suke yi cewar Gwamnatin Kano ta dau gabarar siyar da wani bangare na kwalejin, wanda hakan suka ce kai ya barazana da ci gaban harkar ilmin daliban.

An zargi shugabar makaranta da amsar kudin dalibai

An dage yanke hukunci a shari’ar takardun makarantar Shugaba Buhari

Mahukunta sun rufe makarantar KCC Kano
Wakilin mu Umar Idiris Shu’ibu ya rawaito mana cewa, farfesa Kurawa ya kuma kara da cewa, shakka babu Gwamnatin Kano ko kadan bata dauki wannan mataki ba. A maimakon haka ta maida hankali ne wajen bunkasa sha’anin koyo da koyarwar dalibai.

Shugaban kwalejin ya kuma bada tabbacin gabatar da koken kungiyar ASUP ga Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, don ganin an kare muradan su da suka shafi ci gaban dalibai.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!