Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abinda yasa Jamb ta tilastawa dalibai amfani da lambar NIN

Published

on

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta kasa JAMB ,ta ce a bana babu dalibin da zai rubuta jarrabawar shekara 2020 har sai yana da lambar katin dan kasa wato NIN.

Mai Magana da yawun hukumar Dakta Fabian Benjamin ne ya bayyana haka a jiya Talata a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Lagos.

Fabian Benjamin ya ce manufar shi ne samun cikakkun bayanan dalibi a wani mataki na dakile satar jarrabawa.

Yace hukumar ta JAMB ta yi tsarukan da suka kamata da hadin gwiwar hukumar da ke kula da mallakar katin dan kasa domin samun nasarar al’amarin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!