Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An nada shugabar riko ta ma’aikata tarayya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nada Dakta Folashede Yemi-Esan a matsayin mai rikon mukamin shugabar ma’aikata ta tarayya.

Dakta Folashade Yemi Esan ta maye gurbin Winifired Oyo-Ita wadda ke fuskantar tuhuma sakamakon zargin ta a badakalar sama da naira biliyan uku.

Hakan na kunshe na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labarai a ofishin sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey.

Sanarwar ta ce an bukaci Winifired Oyo-Ita da fara hutu domin bai wa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa EFCC damar gudanar da bincike kan zargin da ake yi mata.

A cewar sanarwar sabuwar mai rikon mukamin shugabar ma’aikatan tarayyar, Folashade Yemi-Esan wadda ita ce babbar sakatariya a ma’aikatar albarkatun man fetur za ta ci gaba da rike mukamin har zuwa lokacin da za a nada cikakken shugabar ma’aikatan tarayya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!