Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An yi musayar wuta tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a Mogadishu

Published

on

Rahotanni daga kasar Somali na cewa an yi musayar wuta tsakanin jami’an tsaro da wasu ‘yan bindiga, sa’ao’i kadan bayan mutuwar sama da mutum talatin, sakamakon tashin bom a jikin wani dan kunar bakin wake a babban birnin kasar Mogadishu.

Kamar yadda rahotanni suka nuna harin da ake zargin kungiyar Al-Shabab ta masu tayar da kayar baya ne suka kaddamar, yayi sanadiyyar lalacewar gine-gine da suka hadar da shaguna da kuma wuraren cin abinci.

Tun farko maharani sun mamaye yankunan da suka kaddamar da harin, inda suka fara harbin kan mai uwa dawabi a babban birnin kasar Mogadishi cikin daren jiya zuwa wayewar asubahin yau.

Sama da mutum sittin ne suka samu munanan raunika, yayinda ake cigaba da kwashe fararen hula a wuraren da gine-gine suka rushe, inda ake ganin cewa akwai yiwuwar samun karin adadin mutanen da suka rasa rayukan su sakamakon harin.

A cewar rahotanni har yanzu jami’an tsaro na cigaba da kai komo a wuraren da maharani suka kaddamar da harin, yayinda ake cigaba da binciko wadanda ginin ya rufta a kan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!