Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Gangar mai miliyan 22 a jihar Edo yayi batan dabo

Published

on

Gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki, ya ce, cikin watanni shidan farko na wannan shekara, barayin ‘Mai’ sun sace gangar mai miliyan ashirin da biyu.

Gwamna Obaseki ya kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki da su tabbata sun yi duk me yiwuwa wajen ganin an dakile matsalar satar danyen mai a kasar nan.

Godwin Obaseki wanda shine shugaban kwamitin wucin gadi na majalisar kula da tattalin arziki ta kasa kan dakile matsalar satar danyen mai, ya ce, lamarin ya yi munin gaske da ya kamata kasar nan ta dau mataki don shawo kan matsalar.

Acewar sa, matukar ba a dauki matakin dakile lamarin ba, to kuwa ba ko shakka, kasar nan za ta yi asara fiye da wanda aka gani a baya, a nan gaba. Gwamnan na jihar Edo yana wannan jawabi ne wajen taron masu ruwa da tsaki da kamfanin mai na kasa (NNPC) ya shirya, a Abuja

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!