Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Asusun lamuna ya shawarci Najeriya samar da hanyoyin bunkasa kudaden shiga

Published

on

Asusun bada lamuni na majalisar dinkin duniya IMF ya shawarci kasar nan da ta lalubo hanyoyin da za ta bunkasa kudaden shigar ta musaman ta bangaren da ba na mai ba.

Mataimakin daraktan da ke kula da bangaren tara kudade na asusun na IMF Poulo Mauro ne ya bayyana hakan ya yin taron hukumar ta IMF da kuma bankin duniya da ke gudana  a birnin Bali na kasar Indonesia.

Ya ce kasar nan ba bukatar sauya dabarun tara kudaden ta daga bangaren mai zuwa wasu bangare na daban sai dai ya ce hakan ba yana nufin kasar nan ta yi hakan da gaggawa ba amma dai akwai bukatar hakan.

Mauro yana wadannan kalamai ne yayin da ya ke maida jawabi kan tambayar  da aka yi masa na cewar wace hanya kasar nan zata bi wajen habaka kudaden harajin ta.

Inda kuma ya amsa da cewar bunkusa bangaren da ba na albarkatun man fetur ba na da matukar muhimmanci, a cewar sa ya kamata a sanya jari mai yawa a bangaren masana’antu da noma

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!