Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Fursunoni 500 ne ke karatu a jami’ar karatu daga gida ta kasa kyauta

Published

on

Shugaban jami’ar karatu daga gida ta kasa NOUN Farfesa Abdallah Uba Adamu ya ce akalla Fursunoni 500 ne yanzu haka ke karatu a jami’ar kyauta.

Farfesa Abdallah Uba ya shaida hakan ne lokacin da ya ziyarci babban sakatare a ma’aikatar Ilimi ta tarayya Mr Sonny Echono bisa rakiyar shugabar sashen harkokin ilimi na kasashen rainon Ingila Farfesa Aisha Kanwar.

Ya kara da cewa ko wane dan kurkuku a Najeriya yana da ‘yancin yin karatu kyauta a jami’ar ta NOUN har zuwa inda ya ke bukata.

Tun da fari a na ta jawabi shugabar sashen harkokin ilimi nakasashe rainon Ingila Farfesa Aisha Kanwar, kira ta yi ga hukumomin kasar nan su tura sabon wakilin kasar nan a hukumar sakamkon karewar wa’adin Hajiya Ladi Katagum ta yi.

Da ya ke mayar da martani babban saktare a ma’aikatar ilimi ta tarayya Mr Sonny Echono cewa ya yi sun ware wani kaso na kasafin kudin ma’aikatar na bana don kula da du wasu bukatun ksar nan a sashen ilimi na kungiyar kasashen rainon ingila, kuma shiri ya yi nisa don tura sabon wakilin kasar nan ga sashen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!