Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin jihar Adamawa za ta kara yawan jami’an tsaro a wuraren da ake fama da matsalolin tsaro

Published

on

Gwamnatin jihar Adamawa ta ce za ta kara yawan jami’an tsaro a wuraren da ake fama da matsalolin tsaro a fadin jihar domin kare rayukan al’umma.

Kwamishinan yada labaran jihar ta Adamawa Alhaji Ahmad Sajoh shi ne ya sanar da haka ga manema labarai a Yolan jihar Adamawa inda ya ce gwamnatin ta dauki wannan mataki ne jim kadan bayan kammala taron gaggawa da jami’an tsaro a jihar domin magance matsalar da ya gudana a jiya Laraba.

Ahmad Sojon ya ce taron wanda mataimakin gwamnan jihar Martins Babble ya jagoranta ya amince da cewa ya kamata a dauki matakin gaggawa domin magance matsalolin da ke addabar jihar.

A cewar sa an kuma umarci hukumar bada agajin gaggawa ta jihar da kuma ma’aikatar lafiya da su samar da abinci da kayan magun-guna ga yankunan da rikicin ya shafa.

Rahotanni sun yi nuni da cewa jihar da Adamawa na fama da rikicin Fulani Makiyaya da manoma musamman a kananan hukumomin Guyuk da Demsa da kuma Numan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!