Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hatsarin mota ya rutsa da wasu dalibai 23 a garin Dandunduru dake karamar hukumar Gaya

Published

on

Hatsarin mota ya rutsa da wasu dalibai 23 da malamansu da suka taso daga karamar hukumar Misau ta Jahar Bauchi zuwa nan Jahar Kano a garin Dandunduru yankin karamar hukumar Gaya da misalin karfe 11:00 na safiyar Talatar nan.

Wani magidanci wanda hadarin ya faru akan idonsa mai suna Ibrahim Adamu ya ce hadarin ya faru ne sakamakon taho mugama da wata mota inda daliban maza 13 da kuma mata 10 suka rasu.

Ibrahim Adamu ya kuma bayyana cewa direbobin motocin biyu suna yin gudu na wuce sa’a ne wanda hakan ne ya haddasa aukuwar mummunan hadarin, inda aka kwashe wadanda suka jikkata aka kai su babban Asibitin garin gaya domin duba lafiyarsu sakamakon munanan raunuka da suka samu .

Jami’in hudda da jamaa na rundunar Yansanda ta Jahar Kano DSP Magaji Musa Majiya inda ya tabbatar da faruwar hadarin inda yace ana nan ana kwashe gawawwakin.

DSP Magaji Musa Majiya ya ce rundunar ‘yan sandan na nan tana kokarin yin abinda ya kamata kan hadari.

Kakakin hukumar kare aukuwar hadurra ta kasa FRSC shiyyar Kano, Kabiru Ibrahim Daura ya bayyana cewa, bayan rasuwar daliban 23 , wasu mutum 3 sun samu raunuka inda yanzu haka mutum 2 ke babban asibitin karamar hukumar Gaya yayin da aka kawo mutum 1 wani asibiti a nan cikin garin kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!