Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar EFCC ta ce zata yi aiki da hukumar NYSC wajen dakile ayyukan bata gari

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), ta ce, za ta rika aiki tare da hukumar kula da masu yiwa kasa hidima (NYSC) wajen dakile ayyukan batagari.

Hukumar ta EFCC ta ce ta karbi korafe-korafe daga hukumar masu yiwa kasa hidima (NYSC), cewa, akwai wasu marasa kishin kasa da suke sayar da takardar shaidar kammala karatun su ga wadanda basu kammala karatu ba wajen gudanar da hidimar kasa.

Mai rikon mukamin shugaban hukumar ta (EFCC), Ibrahim Magu ne ya bayyana haka jiya a birnin tarayya Abuja yayin zantawa da darakta Janar na hukumar masu yiwa kasa hidima Brigadier Janar Shuaibu wanda ya kai masa ziyara ofishin sa.

Anashi bangaren shugaban hukumar masu yiwa kasa hidima brigadier Janar Shu’aibu cewa yayi za su yi duk me yiwuwa wajen ganin an dakile ayyukan batagari.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!