Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Hukumar tace fina-finai ta kasa ta kone fina-finan batsa a Kano

Published

on

Hukumar tace fina-finai ta kasa ta yi kira da ‘yan kasuwa da kamfanonin shirya fina finai dasu mai da hankali wajen inganta harkokin saida fina finai masu mahimmanci da ma’ana a cikin alumma.

Shugaban hukumar  mai kula da shiyyar Kano Alhaji Umar Fagge ne ya bayyana haka lokacin da  suke kona fina-finai na basa a harabar hukumar dake nan kano.

Ya kara da cewa sun kama fina-finai batsa guda dubu biyar a kasuwanin jihar nan domin karkabe bata gari a cikin kasuwanin.

A nasa jawabin hakimin karamar hukumar  Dala Alhaji Abdullahi Lamido Sunusi Turakin Kano ya ce, dole ne iyayen yara su sa ido sosai a irin fina- finai da yaransu suke kallo domin wasu fina-finai suna bata tarbiyar yara.

Wakilin mu Shamsu Da’u Abdullahi ya rawaito cewa shuwagabannin kamfanonin shirya fina-finai da mayan jami’an tsaro sun hallaci kona fina -finai na basa guda dubu biyar.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!