Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotun Koli tayi watsi da karar Atiku

Published

on

Yau Laraba Kotun Koli ta fara sauraron daukaka karar da Atiku Abubakar ya shigar a gabanta, yayin da yake kalubalantar nasarar da Shugaba Muhammadu Buhari ya samu a babban zaben da aka yi a wannan shekara ta 2019.

Sai dai Kotun koli ta yi watsi da karar tun kafin aje ko’ina da jam’iyyar PDP da dan takarar ta, Atiku Abubakar suka shigar suna kalubalantar nasarar da aka bayyana abokin takararsa, Muhammadu Buhari ya yi a zaben da aka gudanar ranar 23 ga watan Fabrairun wannan shekara.

Alkalin Alkalan babbar kotun Najeriya, mai shari’a Tanko Muhammad da ya jagoranci alkalan babbar kotun su shida ya sanar da hukunci kan shari’ar cikin sadarori uku da suka kawo karshen duk wata takaddama kan wancan zabe.

Atiku ya musanta ikrarin jami’yyar APC cewa bai cancanci tsayawa takara ba

Zamfara:rundunar yan sanda ta musanta rahotannin kai hari ga shaidun Atiku Abubakar

Atiku:ya nemi kotu ta ayyana shi ya lashe zabe

Babban Alkalin Alkalan na kasa ya bayyana cewa sai a nan gaba za a bayyana dalilan da ya sanya alkalan suka yanke wannan hukunci.

Ya kara da cewa makonni biyu suka yi shi da sauran alkalan suna karanta dukkan bayanai da kuma shaidun da aka gabatar kan karar, inda suka lura da rashin madogara a karar.

An yanke wannan hukunci da dukkan Alkalan su shida suka amince da shi cikin abin da bai kai Awa guda ba, bayan da kotun ta saurari bayanan daukaka kara daga bakin mai gabatar da kara.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!