Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar kwadago: ba zata amince da kasa da dubu talatin ba a matsayin karanci albashi

Published

on

Shugabancin kungiyar kwadago ta kasa bangaren Joe Ajaero, ta ce, gamayyar kungiyoyin kwadagon kasar nan ba zasu sanya hannu kan duk wata yarjejeniya da gwamnatin tarayya ba game da mafi karancin albashi da ya gaza naira dubu talatin.

Shugaban bangaren kungiyar kwadagon ta United Labour Congress Joe Ajaero ne ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Lagos.

Ya ce, dubu ashirin da hudu ba zai taba kasancewa mafi karancin albashi ba, a don haka ya kamata gwamnati ta sake tunani kan batun.

Ya kuma ce kwamitocin nazarin mafi karancin albashi da suka kammala aikin su a baya-bayan nan, sun amince kan cewa naira dubu talatin ta kasance mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan.

 

Shugaban kungiyar ta United Labour Congress ya nanata cewa ‘yan kwadago a kasar nan ba za su taba amincewa da dubu ashirin da hudu da wakilan gwamnati suka sanar ba

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!