Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai zata sake bincikar dawo da tallafin man fetur

Published

on

Majalisar wakilai ta ce za ta binciki sake dawo da tallafin man fetur da kuma dakile matsalolin da ke janyo karancin mai a kasar nan.

 

Shugaban majalisar Yakubu Dogara ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da mambobin majalisar wadanda suka dawo daga hutun Kirsimeti da sabuwar shekara.

 

Ya ce majalisar za ta yi aiki tukuru domin samar da mafita game da matsalar tsaro dana tattalin arziki da ke addabar kasar nan.

 

Yakubu Dogara ya kuma ce abin damuwa ne matuka yadda aka fuskanci matsalar karancin man fetur a kasar nan a karshen shekara.

 

Yana mai cewar dalilan da suka sanya suka goyi bayan kara kudin litar mai daga naira tamanin da bakwai zuwa dari da arba’in da biyar shine tabbatar musu da aka yi cewa za a cire tallafin mai.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!