Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar zartawa gwamnatin tarayya ta amince da fitar da fiye da naira biliyan 185

Published

on

Majalisar zartarwar gwamnatin tarayya ta amince da fitar da naira biliyan 185 da miliyan 272 domin ayyuakan gyara da kuma gina sabbin hanyoyi goma sha hudu a fadin kasar nan.

 

Mashawarci na musamman ga shugaban kasa kan kafafen yada labarai Femi Adesina ne ya sanar da hakan ga manema labarai jim bayan kammala zaman majalisar zartarwar na jiya.

 

Ya kuma bayyana wasu daga cikin hanyoyin da za a gina da kuma yiwa gyara da suka hadar da hanyar da ta tashi daga Goza zuwa Dambowa zuwa Goniri zuwa Ngamdu dake jihar Yobe da kuma Borno.

 

Sai kuma hanyar da ta tashi daga Mayo Balwa zuwa Jada zuwa Ganye zuwa Torngo da ke jihar Adamawa, sai kuma hanyar da ta tashi daga Ado zuwa Ifaki zuwa Otun da ke kan iyakar jihar Kwara da kuma Ekiti

 

Haka kuma ya ce an kammala dukkanin wasu shirye-shirye domin sanya hannu akan kasafin kudin wannan shekarar da shugaban kasa zai yi nan da yan kwanaki masu zuwa

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!