Labarai
Masu garkuwa da mutane sun sace dan jaridar Borno
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/11/Abdulkarim-Haruna-.jpeg)
Wasu ‘’Yan garkuwa sun sace wani dan jarida da ke aiki da gwamnatin jihar Borno, Abdulkarim Haruna.
An dai sace wannan dan jarida ne a a jiya litinin da misalin karfe uku zuwa hudu na yammancin jiya, a yayin da yake tafiya daga babban birnin tarayya Abuja zuwa jihar Bauchi.
Abdulkarim Haruna dai ya hau motar Bauchi daga tashar Nyanya a Abuja, tuni dai direban motar ya kai jakarsa da wayarsa ofishin yan sanda dake Jagindi a jihar Kaduna.
Direbar motar ya ce masu garkuwar na sanye da kayan sarki inda suka dauke dan jaridar