Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Matashi dan shekara 20 ya nutse a kogin Bachirawa

Published

on

Wani matashi dan shekara 20 da haihuwa ya nutse a yayin da yake wanka  a kogin Bachirawa -Darewa dake yankin karamar hukumar Ungogo a nan jihar Kano

 

Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano Malam Sa’idu Mohammad ne ya bayyana afkuwar alamarin inda ya ce matashin ya nutse a kogin ne a ranar lahadi bayan da suka je wanka.

 

Rahotanni sun bayyana  cewar wani mazaunin unguwar Malam Abdulrahma Adamu , ya ce al’amarin ya faru ne da misalin karfe 12.45 na rana, inda aka tsinci gawar matashi iliyasu, ya kara da cewa suna samun labarin suka garzaya domin ceto matashin, amma ina rai yayi halin sa.

 

Suna isa kogin da misalin karfe daya na rana ko da suka isa sai gawar matashin aka tsamo, tuni suka mikawa mai unguwar Zango Barebari Alhaji Ahmad Isa  gawar matashin.

 

A ranar 5 ga watan Satumban wannan shekara ne dai  aka sami rahoton wani matashi dan shekara 16 Shahid Lawal ya nutse a kogin na Bachirawa-ramin  Kasa dake karamar hukumar Fagge a yayin da yake wanka

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!