Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun samar da taransifomomi guda 500 a kano – kwamshinan raya karkara

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta samar da taransifomomi guda 500 a faɗin jihar, domin samar da hasken hutar lantarki a birni da karkara.

Kwamishinan Raya karkara da bunƙasa birane Alhaji Abbas Sani Abbas ne ya bayyana haka yayin ganawarsa da manema labarai a ofishinsa.

Alhaji Abbas Sani Abbas ya ƙara da cewa gwamnati zata saka taransifomomin ne a kauyuka da birane da kuma yankunan da suke fuskantar matsalolin hasken lantarki a cikin kwaryar birnin Kano.

Abbas ya kuma ce ma’aikatarsa za ta samar da rijiyoyin burtsatse guda dubu biyar a kananan hukumomi 44 dake faɗin kano domin magance matsalar karancin ruwan sha.

Haka kuma kwamshinan Ya yi kira ga al’ummar jihar Kano dasu koyi dabi’ar alkinta kayan gwamnati kasancewar gwamnati tana samar da kayan ne domin cigabansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!