Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar yan sandan jihar Akwa Ibom ta musanta cewa tana da hannu a rikicin majalisar dokokin jihar

Published

on

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Akwa Ibom Musa Kimo ya musanta cewa rundunar ‘yan sandan jihar na da hannu wajen rikicin da majalisar dokokin jihar ta fada tun daga ranar 19 ga wannan wata.

Musa Kimo ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi ga manema labarai kan rikicin da ya afko na ranar 27 bayan da aka garkame majalisar.

A cewar sa jami’an ‘yan sanda za su gudanar da ayyukan su ba tare da nuna son zuciya ba ga kowanne bangare.

Haka zalika kwamishinan ‘yan sanda ya gargadi ‘yan siyasa da magoya bayan jam’iyyu a jihar ta Akwa Ibom da su guji tada hautsani da rikici da sauran ayyukan ta’addanci, don kawo zaman lafiya a jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!