Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Sashen kula da albarkatun man fetur ya musanta zargin cewar an bada lasisi guda 38

Published

on

Sashen kula da Albarkatun man fetur na kasa DPR, ya musanta rahotannin da kafafen yada labaran kasar nan suka yada cewa, ya ba da lasisi guda 38 ga ‘yan kasuwa masu zaman kansu domin kafa kananan matatun mai.

A cewar DPR lasisi 25 kacal ya ba da ba 38 ba kamar yadda aka yi ta yadawa tun da fari.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sashen ya aikewa manema labarai jiya a Abuja.

A cewar sanarwar daga shekarar 2002 zuwa yanzu masu sha’awar gina kananan matatun mai 105 ne suka mika da bukatar su.

Sashen kula da Albarkatun man fetur din ta cikin sanarwar dai, ya kuma ce, an baiwa ‘yan kasuwar wa’adin watanni goma sha takwas ne domin kammala aikinsu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!