Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Wani Baturen ‘’Yansanda ya taba karya malamin makaranta saboda ya mallaki sabuwar mota

Published

on

Farfesa Sadiq Isa Rada tare da Ado Sale Kankiya

Tun kafa kungiyar kwato hakkin dan Adam ta network for justice a shekaru 26 da suka wuce ta yi sanadin ceto mutane da dama daga kangin zalunci.

Tsohon shugaban kungiyar kuma mamba a yanzu Farfesa Sadiq Isa Rada ne ya bayyana haka a tattaunawa da yayi da shirin Barka da Hantsi na nan gidan rediyan Freedom.

Sadiq Isa Rada yace akwai wani lokaci da wani jami’in dansanda ya karairaya wani malamin makaranta sakamakon ya sayi sabuwar mota.

Farfesa Rada yace dalilin da yasa baturen ‘’yansandan dake aiki a garin Daura ta jahar Katsina ya karya malamin shi ne yana ganin bashi da damar da zai iya sayan sabuwar mota.

Yace sun taba nemawa wani direba hakkin sa lokacin da wani soja ke cikin maye ya taka wani direba.

Farfesa Rada ya kara da cewa kungiyar ta network for justice Farfesa Attahiru Jega ne da Farfesa Auwalu Hamisu Yadudu da Farfesa Na’iya Sada da Bala Abdullahi suka kafa ta.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!