Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Za mu fara koyar da aikin kula da lafiya a jami’ar Yusuf Maitama Sule – Farfesa Kurawa

Published

on

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ce za ta bude tsangayar koyar da aikin lafiya a Jami’ar a shekara mai kamawa ta 2022.

Shugaban Jami’ar Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa ne ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da sababbin daliban makarantar su dubu biyar da sittin, da ta dauka a zangon karatu na shekarar 2021/2022.

Ya ce Jami’ar za ta ci gaba da baiwa dalibanta ilimin da ya dace wanda daliban za su yi amfani da shi da zai taimaki kasar nan.

Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa ya bukaci daliban da su zama jakadu na gari a ciki da wajen makarantar yayin da suke gudanar da karatun su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!