Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu tabbatar mun gyara dukkannin cibiyoyin koyar da sana’ar hannu dake fadin kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta yi alƙawarin kammala aikin gyara dukkannin Makarantun fasaha dana horar da sana’o’in dogaro da kai da aka samar da su a shekarar 2011 a ƙananan hukumomi 44 nake faɗin jihar

Gwamnan jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan a yau yayin bikin ranar baje kolin fasahar matasa ta duniya da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake ƙaramar hukumar Dawakin kudu haɗin gwiwa hukumar kula ilimin ƙananan yara ta duniya UNESCO.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce reƙe sana’o’in hannu wani jigo ne da zai bunƙasa aiyukan masana da samarwa da matasa aiyukan yi.

A nasa jawabin karamin ministan ma’aikatar cigaban matasa Mr. Ayodele Olawode ya yaba da harkokin cibiyar, inda ya ce ma’aikatar sa ta fito da shirin ilimartar da matasa miliyan 7 akalla sana’o’in dogaro da kai.

Da yake jawabin Shugaban Hukumar UNESCO ta ƙasar nan Abulrahman Diyalo ya ce za su yi haɗin gwiwa da gwamnatin jahar kano da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote domin koyar da dubban matasa sana’o’in dogaro da kai.

Haka kuma gwamnan ya yi alƙawarin samarwa da cibiyar gidajen kwanan dalibai da biya musu kudin karatu da daukar nauyin kai su makaranta a kullum da kuma kulawa da walwalarsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!