Connect with us

Labarai

Ƴan bindiga sun hallaka sama da mutane 30 a jihar Neja

Published

on

Bayanai daga jihar Neja da ke arewa ta tsakiyar Najeriya na cewa wasu ƴanbindiga sun kai hari jihar, inda suka kashe sama da mutum 30 tare da sace wasu da dama.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya aike wa BBC ya ce ƴanbindigar waɗanda ake zargi sun fito daga dajin Kabe sun far wa Kasuwan-Daji da ke ƙauyen Demo da maraicen ranar Asabar, inda suka ƙona kasuwar tare da lalata shaguna da sace kayan abinci.

Sanarwar ta ci gaba da cewa da safiyar yau Lahadi ne haɗin gwiwar tawagar jami’an tsaro suka ziyarci yankin, kasancewar sun samu rahoton harin cikin dare.

”A lokacin ziyarar jami’an tsaron sun tarar da sama da mutum 30 da ƴanbindigar suka kashe, yayin da suka samu labarin sace wasu”, a cewar sanarwar.

Jami’an tsaron sun tabbatar da cewa suna bakin ƙoƙarinsu don ganin sun kuɓutar da mutanen da ƴanbindigar suka sace.

Jihar Neja na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da hare-haren ƴanbindiga.

Ko a watan Nuwamban shekarar da ta gabata ma wasu mahara sun far wa makarantar sakandiren Papiri tare da sace ɗalibai fiye da 300, kodayake daga baya sun sako su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!