Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ɗan jarida tamkar malami yake wajen faɗakarwa – Majalisar malamai

Published

on

Majalisar malamai ta jihar Kano ya bayyana cewa aikin jarida ya yi kama da aikin malanta ta fannin faɗakarwa.

Shugaban majalisar Malam Ibrahim Khalil ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Freedom Radio.

“Ni dai abin da na sani a aikin jarida kamar ko wanne aiki ne akwai daidai akwai kuskure, kuma aikin jarida ya yi kama da aikin malami amma shi ɗan jarida bambamcin sa da malami shi ne gina ɗan adam yadda zai riƙa tunani shi kuma dan jarida zai kawo ma abin da za ka yi tunani a kan sa” in ji Malam Ibrahim.

Malam Ibrahim Khalil ya kuma ce, “Sai ana yin amfani da ƴan jarida wajan haifar da futuntunu, su kuma dama aikin jarida asali ƴan hamayyane suka kafa ta sannan su kuma aikin ƴan jarida kullum sukan fito da abin da zai ɗau hankalin mutane”.

Malamin ya yi zargin cewa akwai kura kurai da ‘yan jarida suke yi wanda su kan su suna kaucewa ƙa’ida.

“Amma futuntuni suna afkuwa ne daga abubuwa daban-daban ba zaka kama Ƴan jarida ɗari bisa ɗari kace sune suke haifar da futuntunu ba, ni dai abin da nasani aikin jarida kamar ko wanne aiki ne akwai daidai akwai kuskure”.

 

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!