Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NAHCON zata samo sabon kamfanin jigilar alhazai

Published

on

Hukumar aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta kafa wani kwamiti da zai nemo wani sabon kamfanin da zai yi hidima ga alhazan kasar a lokacin aikin hajjin shekara mai zuwa ta 2024.

Shugaban hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan, ne ya bayyana hakan a jiya alhamis yayin taron lakca da bada lambar yabo da aka shirya a Abuja.

A cewar Zikirullah, ana sa ran kwamitin da aka kafa zai samar da wasu hanyoyi da za a bi domin kyautatawa mahajjata kafin aikin hajjin shekara mai zuwa.

‘Haka zalika an raba guraben aikin hajji ga hukumomin jin dadin alhazai na jihohi domin fara shirye-shiryen aikin hajjin badi akan lokaci’.

A baya dai Alhazan kasar sun koka kan rashin yi musu hidima yadda ya kamata da wasu kamfanonin Saudiyya ke yi.

Rahoton: Abdulkadir Haladu Kiyawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!