Labarai
Gwamnatin Adamawa ta rushe rumfuna da shagunan da aka gina ba bisa ka’ida ba a kasuwar Jimeta

Gwamnatin jihar Adamawa ta rushe rumfuna da shagunan da aka gina ba bisa ka’ida ba a cikin babbar kasuwar Jimeta da ke birnin Yola.
Wannan mataki ya biyo bayan umarnin da gwamnan jihar, Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayar domin dawo da kasuwar yadda take a baya.
Rahotanni sun nuna cewa an gudanar da aikin rushewar ne da nufin wanzar da tsari, da kawar da cunkoso da gina guraren kasuwanci ba tare da izini ba, wanda ke hana walwalar ’yan kasuwa da masu siyayya.
Gwamnatin ta ce za a ci gaba da irin wadannan matakan domin tabbatar da doka da oda a manyan kasuwanni da tituna a fadin jihar.
You must be logged in to post a comment Login