Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta cigaba da sauraron shari’ar Malam Shekarau

Published

on

A yau ne babbar kotun tarayya dake zaman ta a Kano ta dage ci gaba da sauraran karar da ake tuhumar Malam Ibrahim Shekarau da wasu mutum biyu.

Babbar kotun tarraya dake zaman ta a kano taci gaba da sauraran karar da gwamnatin tarraya ke tuhumar Malam Ibrahim Shekarau da Aminu Bahir Wali da Mansur Ahmed da ake zargin su da sama da fadi da kimanin kudi naira miliyan dari tara da hamsin na jamiyyar PDP.

A cikin kudin Malam Ibrahim Shekarau ya karbi naira miliyan asirin da biyar da Mansur Ahmed shima ya karbi naira miliyan asirin da biyar daga cikin naira miliyan dari tara da hamsin.

Babban alkalin dake jagorantar karar Mai sharia Lewis Algbon na babbar kotun tarayya yace wanda ake zargi suna da damar kawo shedun da za su kare su.

Babban jamin dake wakiltar hukumar hana cin hanci da rashawa ta EFCC yace kasha kudin baa bi kaidar daya kama ta ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!