Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Masu zanga-zanga a Papua sun lalata gine-ginen da dama

Published

on

‘Yan sanda a kasar Indonesiya, sun ce, masu zanga-zanga a lardin Papua da ke kasar, sun lalata gine-gine da safiyar yau litinin.

Zanga-zangar da aka fara tun a watan Agustan da ya gabata, ta yi sanadiyar mutuwar mutane biyar a lardunan Papua da kuma Papua ta yamma.

Rahotanni sun ce zanga-zangar ta samo asali ne biyo bayan zargin nuna wariya da jami’an tsaro ke yi ga dalibai ‘yan asalin lardin Papua a tsibirin Java.

Kafofin yada labaran kasar sun ruwaito cewa, masu zanga-zangar sun cinna wuta ga ofishin hukumomi da ke Wamena.

Mai Magana da yawun rundunar ‘yan sandan kasar ta Indonesiya, Dedi Prasetyo, ya ce, tuni aka tura da jami’an tsaro domin dawo da doka da oda.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!