Connect with us

Labarai

Akwai  yiwuwar zan fafata da Tinubu a zaɓen 2027- Rotimi Amaechi

Published

on

Tsohon ministan sufuri a gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, Rotimi Amaechi, ya ce akwai  yiwuwar zai  fafata  da Shugaba Tinubu a zaɓen shekarar 2027. 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito  cewa tsohon gwamnan na jihar Rivers ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi, a baya bayan nan. 

Amaechi, wanda ya zo na biyu a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC wanda ya samar da Tinubu a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a 2022, ya ce bai cire yiwuwar tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2027 ba, yana mai cewa lokaci ne zai nuna hakan. 

Bayanin nasa  na zuwa ne ƙasa da wata guda bayan shugabannin APC sun amince da Tinubu a matsayin ɗan takara guda ɗaya na jam’iyyar a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. 

Shugabannin adawa da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da  ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, kana tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da wasu da dama, suna ƙoƙarin kafa haɗaka don ganin sun kayar  da Tinubu a  zaben 2027.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!