Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Al’umma na da damar yin kiranye ga wakilan su- Barista Turmuzi

Published

on

Wani lauya a nan kano, Barista Sale Muhammad Turmuzi, ya ce, jama’a suna da ‘yancin yin kiranye ga wakilansu da ke jiran hukuncin kotu, bayan daukara kara a kotu ta gaba, bisa wani zargin cin hanci da rashawa.

Barista Sale Muhammad Turmuzi, ya bayyana hakan ne ta shirin Muleka mu gano na musamman na nan tashar freedom Rediyo da ya gudana a daren jiya.

Batista Sale Turmuzi, ya kara da cewa, a tsarin yadda doka ta tanada, duk wani dan majalisa da ya rasa kaso daya bisa uku na zaman majalisa zai iya rasa kujerarsa matukar bashida kwararan hujjoji.

A daina siyasar uban gida a Najeriya domin cigaban demokradiyya -Farfesa Kamilu

Shugaba Buhari yayi ganawar sirri da wasu tawagar yan siyasa daga Kano

Sale Muhammad Turmuzi, ya kuma ce, an samu gagarumin ci gaba a bangaren yaki da cin hanci da rashawa a fadin kasar nan musamman a bangaren shari’a, bisa yadda ake ganin Kotuna a wannan lokaci suna yanke hukuncin da ke turawa da masu rike da mukaman siyasa zuwa gidan gyaran hali.

Muhammad Sale Turmuzi, ya kuma nanata cewa, zartas da hukuncin zaman gidan gyaran hali kan tsoffin gwamnoni kuma sanatoci masu ci kan cin hanci zai taimaka gaya wajen karfafa mulkin dimukuradiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!