Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Al’ummar jihar Adamawa na dakon shugaba Buhari

Published

on

Rahotanni daga jihar Adamawa na cewa yanzu haka dai al’ummar Yola na dakon zuwan shugaban kasa Muhammadu Buhari gobe talata.

Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da wasu manyan ayyuka da dama, tare da gabatar da jawabi yayin wani taro na musamman da gwamnatin jihar ta shirya kan yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar rahotanni yanzu haka dai an kawata birnin Yola da fenti hadi da manyan alluna dake nuna maraba da zuwan shugaba Muhammadu Buhari.

A wata sanarwa da ya fitar, mataimakin gwamnan jihar Mista Martins Babale, wanda kuma shine shugaban kwamitin da ya shirya taron, yace gwamnatin jihar ta gama shiryawa tsaf domin karbar bakuncin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Ya bayyana cewa taron mai taken rawar da gwamnati take takawa, ana sa ran mukaddashin shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu da takwaran sa na hukumar yaki da cin hanci da rashawa ICPC farfesa Bolaji Owasanoye zasu gabatar da jawabi.Al

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!