Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Amaechi ya karya ta labarin ya tsallake rijiyar da baya

Published

on

Ministan sufurin Rotimi Amechi ya karyata labarin da ake yadawa cewa ya tsallake rijiya da baya, bayan da masu satar mutane suka kaiwa jirgin kasa hari a Mando dake jihar Kaduna, da yammacin jiya Lahadi.

Rotimi Amechi ya wallafa hakan a shafin sa na Twitter cewa labarin karya ce tsagwaran ta, a don haka al’umma su yi watsi shi.

Rahotanni sun bayyana cewar, a jiya Lahadi ne masu satar mutane suka yi artabu da jami’an tsaro dai-dai lokacin da fasinjoji za su sauka a tashar jirgin kasa dake Rigasa.

Sai dai da safiyar yau ministan ya karya ta cewa yana cikin jirgin dai-dai lokacin da aka kai harin.

Wata majiya mai karfi daga tashar jirgin kasan ta Kaduna ta tabbatarwa da Freedom Radio afkuwar harin, amma bayan da ministan sufurin ya sauka daga jirgin kasar ne.

Labarai masu alaka:

Kotu tayi watsi da bukatar soke sabbin masarautu

Muhimman abubuwan dake faruwa yanzu haka a Kannywood

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!